DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sufeta Janar na ‘yan sandan Nijeriya ya bada umurnin bincike kan zargin cin zarafi da hallaka masu zanga-zanga da Amnesty International ta yi

-

 

Sufeta Janar na ‘yan sandan Nijeriya Kayode Egbetokun, ya bayarda umurnin yin bincike kan zarge-zargen cin zarafi da kisa da kuma kama masu zanga-zangar matsin rayuwa da ta faru a fadin kasar.
Kungiyar kare hakkin bil adama ta Amnesty International a cikin wani rahoto da ta fitar a kwanannan, ta zargi rundunar ‘yan sanda da amfani da karfin da ya wuce iyaka a yayin zanga-zangar matsin rayuwa da ta faru daga 1 zuwa 10 ga watan Augustan 2024, da yayi sanadiyar mutuwar mutum 24 a jihohin Borno, Kaduna, Kano, Katsina, Jigawa da kuma Niger.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ACP Olumiyiwa Adejobi ya fitar a Abuja, ya ce akwai alamun shakku da kuma karya a zargin da Amnesty International ta yi, inda ya ce Kayode Egbetokun ya bada umurnin yin bincike domin gano gaskiyar lamari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Rukunin farko na maniyyatan jihar Bauchi a Nijeriya, sun tashi zuwa Saudiyya- NAHCON

Hukumar aikin Hajji ta Nijeriya ta bayyana cewa maniyyata 2,520 ne daga cikin jihar Bauchi za su halarci aikin Hajjin bana na 2025 a kasar...

An saki ‘Yan jaridar Sahara FM da aka tsare a Agadez

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na nuna cewa an saki ‘yan jarida uku na gidan rediyon Sahara FM da ke Agadez bayan da aka tsare su...

Mafi Shahara