DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Rukunin farko na maniyyatan jihar Bauchi a Nijeriya, sun tashi zuwa Saudiyya- NAHCON

-

Hukumar aikin Hajji ta Nijeriya ta bayyana cewa maniyyata 2,520 ne daga cikin jihar Bauchi za su halarci aikin Hajjin bana na 2025 a kasar Saudiyya, domin sauke farali.

jaridar the Cable ta rawaito cewa a yayin bikin bankwana da aka shirya a cibiyar Alhazai ta Sultan Sa’ad da ke Bauchi, Gwamna Bala Abdulkadir Mohammed, ta bakin Mataimakinsa, Rt. Hon. Mohammed Auwal Jatau, ya shawarci mahajjatan da su yi amfani da lokacinsu wajen ibada da neman rahamar Allah a kasa mai tsarki.

Gwamnan ya bayyana cewa gwamnati ta dauki nauyin shirya masauki mai inganci wanda ke kusa da Masallacin Harami tare kuma da tabbatar da cewa duk wani shiri da ya shafi kiwon lafiya, sufuri da kula da lafiyar mahajjata ya kammala, domin tabbatar da ingantaccen aikin hajji.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara