DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An saki ‘Yan jaridar Sahara FM da aka tsare a Agadez

-

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na nuna cewa an saki ‘yan jarida uku na gidan rediyon Sahara FM da ke Agadez bayan da aka tsare su a ofishin ‘yan sanda na tsawon lokaci.

Sakin nasu ya zo ne bayan gabatar da su gaban alkali a kotun jihar Agadez a yau Juma’a, inda aka saurari batunsu bisa zargin da ake musu da kuma irin aikinsu na jarida.

Wannan na zuwa ne kasa da makonni biyu da aka gudanar da bikin ranar ‘yancin ‘yan jarida ta shekarar 2025, kan yadda hukumomin tsaro ke mu’amalantar ‘yan jarida a sassan duniya, musamman a yankunan da ke fama da rikice-rikice.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara