Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na nuna cewa an saki ‘yan jarida uku na gidan rediyon Sahara FM da ke Agadez bayan da aka tsare su a ofishin ‘yan sanda na tsawon lokaci.
Sakin nasu ya zo ne bayan gabatar da su gaban alkali a kotun jihar Agadez a yau Juma’a, inda aka saurari batunsu bisa zargin da ake musu da kuma irin aikinsu na jarida.
Wannan na zuwa ne kasa da makonni biyu da aka gudanar da bikin ranar ‘yancin ‘yan jarida ta shekarar 2025, kan yadda hukumomin tsaro ke mu’amalantar ‘yan jarida a sassan duniya, musamman a yankunan da ke fama da rikice-rikice.