DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Nijeriya da makwabtan kasashe sun soma fatattakar Lakurawa

-

Nijeriya da Nijar, da kuma Chadi da wasu makwabtan kasashe sun yi haɗaka wajen fatattakar ‘yan kungiyar Lakurawa da suka addabi iyakokin kasar.
Wannan hadakar na da manufar kakkabe ‘yan ta’addan da ke aiwatar da miyagun ayyuka a kasashen Nijeriya da kasashen dake kewaye da ita.
 
Da yake karin haske akan matakan da suke dauka, daraktan yada labarai na hedkwatar tsaron Nijeriya Manjo-Janar Edward Buba, ya shaidawa jaridar Punch cewa hadin gwuiwar kasashen wajen sintiri akan iyaka zai rufe duk wata mafaka da Lakurawa za su bi domin shiga kasashen.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Alƙali ya yi barazanar soke belin Abdulrasheed Maina da ake zargin kan zambar N738.6m

Babbar Kotun Babban Birnin Tarayya (FCT) da ke Abuja, ta yi barazanar soke belin tsohon shugaban kwamitin garambawul a harkar fansho na ƙasa, Abdulrasheed Maina,...

Majalisar dattawa ta musanta ƙin amincewa da aika sakamakon zaɓe ta na’ura

Bangaren ’yan adawa a Majalisar Dattawan Nijeriya ya fayyace a ranar Alhamis cewa Majalisar ba ta ƙi amfani da tsarin tura sakamakon zaɓe ta na’ura...

Mafi Shahara