DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta yanke wa masu garkuwa da mutane hukuncin kisa a Jigawa

-

Kotu ta yanke wa masu garkuwa da mutane hukuncin kisa

Wata babbar kotu a Jihar Jigawa ta yanke wa wasu masu garkuwa da mutane hukunci  kisa ta hanyar rataya.

Da ya ke zartar da hukunci alkalin kotun mai shari’a Mohammed Musa Kaugama ya ce an sami mutanen biyu da laifuka bakwai da suka hada da yin garkuwa da mutune da hada baki da fashi da makami da haura gidan mutane.

A ranar 21 ga watan Yunin 2021 ne mutanen biyu wato Sani Mohammed da Babannan Saleh, dauke da makami suka haura gidan Hamidi Abdu da ke garin Shangel a karamar Hukumar Ringim inda suka kwace masa kudade masu yawa sannan suka ta fi da shi, daga baya suka nemi kudin fansa har naira miliyan 12 kafin su sake shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Farashin buhun shinkafar waje mai nauyin 50KG ya koma N58,000 a wasu sassan Nijeriya in ji wani rahoton da majiyar DCL Hausa ta Punch ta wallafa.

Rahoton da kamfanin S&P Global ya fitar ya bayyana cewa farashin buhun shinkafa mai nauyin kilo 50 ya sauka zuwa N58,000 a wasu yankunan Najeriya,...

‘Yan siyasar da ke neman mukamai ba don talakawa suke yi ba – Zargin Bafarawa ga ‘yan siyasar Nijeriya

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya yi zargin cewa an yi wa siyasar adawa kamshin mutuwa a Najeriya. Bafarawa, wanda ya kasance jigo...

Mafi Shahara