DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar ECOWAS ta matsa kaimi domin samar da kudin bai daya ga mambobin ta

-

 

Google search engine

Kungiyar ECOWAS ta matsa kaimi domin samar da kudin bai daya ga mambobin ta

Kungiyar ci gaban kasashen yammacin Afrika ECOWAS ko kuma CEDEAO, na ci gaba shirye-shirye kaddamar da kudin bai daya a yankin mai suna ECO, biyo bayan cimma matsayar da aka yi a yayin taron kasashen karo na 65.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwar karshen taron da shugabannin  kasashen suka gudanar karo na 66 a tarayyar Nijeriya Abuja.

A baya dai kungiyar ECOWAS dake da kasashe 15, ta shirya kaddamar da kudin ECK a shekarar 2020, amma cutar korona ta kawo tsaiko inda a halin yanzu aka sanya 2027 a matsayin ranar kaddamarwa.

Hukumar ta ce ta yi amfani da shawararin da babban kwamiti ya gabatar, na zabar kasashe da za a kaddamar da tsarin da kuma wadanda za su shigo daga baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnan Bauchi ya sanya hannu kan dokar kirkirar sabbin masarautu 13 a fadin jihar

Gwamnan Bauchi Bala Muhammad ya sanya hannu kan dokar kirkirar sabbin masarautu 13 a fadin jihar. Daily Trust ta ruwaito cewa a lokacin da yake sanya...

Kenya da Senegal sun kulla yarjejeniyar shige da fice ba tare da biza ba

Gwamnatocin Kenya da Senegal sun bai wa juna damar shige da fice ga 'yan kasashensu ba tare da biza ba na tsawon kwanaki 90. DW Africa...

Mafi Shahara