DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamna Abba ya zargi ‘yan adawa da rura wutar rikicin siyasa a Kano

-

Engineer Abba Kabir Yusuf 

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya zargi jam’iyyun adawa da rura wutar rikicin siyasa a Jihar.

Gwamnan ya yi wannan zargi ne lokacin da ya ke zantawa da manema labarai yayin taron majalisar zartarwar jihar a ranar Laraba, har ma ya bayyana aniyarsa ta daukar tsauraran matakan da suka dace don dakile sake barkewar ‘yan daba a Jihar. 

Wannan dai ya biyo bayan rikicin baya-bayan nan da ya barke tsakanin wasu da ake zargin ’yan bangar siyasa ne a Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saki ‘Yan jaridar Sahara FM da aka tsare a Agadez

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na nuna cewa an saki ‘yan jarida uku na gidan rediyon Sahara FM da ke Agadez bayan da aka tsare su...

Kwamishinan Jigawa ya mayar da rarar Naira miliyan 301 daga kudaden da aka ware don shirin ciyar da al’umma a watan Ramadan

Kwamishinan ayyuka na musamman na jihar Jigawa, Alhaji Auwalu Danladi Sankara, ya mayar da Naira miliyan 301 zuwa baitul malin jihar, daga cikin Naira biliyan...

Mafi Shahara