DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ministan Abuja Wike ya kwace filayen tsohon shugaban kasa Buhari, Tajudeen Abbas, George Akume da wasu manyan mutane 759

-

Ministan babban birnin tarayya Abuja Nyesom Wike, ya kwace filaye tsohon shugaban kasa Muhammad Buhari, da kakakin majalisar dokoki Tajudeen Abbas da kuma Sakataren gwamnatin tarayya George Akume.
Hakama Wike ya kwace filayen wasu manyan mutane da kungiyoyi 759 a yankin Maitama II, Abuja saboda saboda kin biyan kudaden takardar mallaka.
Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa har biyu da hukumar kula da babban birnin tarayya Abuja ta aikewa gidan talabijin na Channels.
Daya sanarwar ta ce, ministan ya yi barazanar kwace filayen jagoran marasa rinjaye na majalisar wakilai Kingsley Chinda da tsofaffin shugabannin majalisar dattawa Iyorchia Ayu da Ameh Ebute da mai tsawatarwa na majalisar dattawa Tahir Monguno; kazalika da wasu sanannun mutane 610, idan har ba su biyu kudaden ba cikin makonni biyu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kungiyar Lauyoyi ta Nijeriya ta bukaci gwamnatin tarayya ta dakatar da aiwatar dokokin haraji

Ƙungiyar Lauyoyin Nijeriya (NBA) ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta dakatar da aiwatar da sabbin dokokin haraji, tana mai cewa rikice-rikicen da suka...

Babu wasu sauye-sauye a dokokin haraji – Gwamnatin Nijeriya

Gwamnatin Nijeriya ta jaddada cewa salo guda ɗaya ne kacal sahihi na sabbin dokokin gyaran haraji da aka rattaba wa hannu, tare da musanta zargin...

Mafi Shahara