DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ministan Abuja Wike ya kwace filayen tsohon shugaban kasa Buhari, Tajudeen Abbas, George Akume da wasu manyan mutane 759

-

Ministan babban birnin tarayya Abuja Nyesom Wike, ya kwace filaye tsohon shugaban kasa Muhammad Buhari, da kakakin majalisar dokoki Tajudeen Abbas da kuma Sakataren gwamnatin tarayya George Akume.
Hakama Wike ya kwace filayen wasu manyan mutane da kungiyoyi 759 a yankin Maitama II, Abuja saboda saboda kin biyan kudaden takardar mallaka.
Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa har biyu da hukumar kula da babban birnin tarayya Abuja ta aikewa gidan talabijin na Channels.
Daya sanarwar ta ce, ministan ya yi barazanar kwace filayen jagoran marasa rinjaye na majalisar wakilai Kingsley Chinda da tsofaffin shugabannin majalisar dattawa Iyorchia Ayu da Ameh Ebute da mai tsawatarwa na majalisar dattawa Tahir Monguno; kazalika da wasu sanannun mutane 610, idan har ba su biyu kudaden ba cikin makonni biyu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za a iya kawo karshen matsalolin Arewa aka hada kai – Uba Sani

Gwamnan Kaduna, Uba Sani, ya ce Arewacin Nijeriya na da kwararru da hazikan ‘yan kasa da za su iya magance matsalolin ci-gaba da ake fama...

Halin kuncin da ‘yan Nijeriya ke ciki ne zai yanke wa Tinubu hukunci a zaben 2027 – NNPP

Jam’iyyun hamayya na NNPP da ADC reshen jihar Osun sun ce halin tsananin talauci da ake ciki yanzu shi ne zai yanke wa shugaban Nijeriya...

Mafi Shahara