DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Rahoton IMF na 2024 ya cire Nijeriya daga ƙasashe 10 da suka fi tarin bashi

-

Sabon rahoton jami’an Hukumar Bayar Da Lamuni Ta Duniya (IMF) ya nuna ƙasashen Afrika da aka fi bi bashi a shekara ta 2024 inda ya bayyana ƙasar Misira a matsayin wacca take da bashi mafi girma a Afrika da ya zarce Dalar Amurka Biliyan 9. 
Rahoton ya nuna cewa a tsakanin watan Janairu zuwa Jun na wannan shekarar ta 2024, gwamnatin Najeriya ta biya sama da Dalar Amurka Biliyan 2.24 na basukan da ake bin ƙasar wandanya fitar da ita daga ƙasashen da bashin yayi musu ƙatutu. 
Rahoton da ofisin kula da basussuka na Najeriya ya fitar ya nuna cewa a watanni 3 na farkon shekarar nan ta 2024, gwamnatin Najeriya ta biya Dalar Amurka Biliyan 1.12 na bashin da ake bin ta. A watanni 6 na shekarar ta dake biyan Dalar Amurka Biliyan 1.12 ga ƙasashe fa kuma hukumomin da ke bin ta bashi da suka haɗa da IMF da Babban Bankin Duniya. 
Wannan cigaban ya samu ne sakamakon matakin da gwamnatin Tinubu ta ɗauka na dena almubazzaranci da kuɗaɗen ƴan ƙasa musamman cire tallafin Man Fetur wanda ya taimaka wajen samun ƙarin kudade ga Jihohi da ma ƙasar baki ɗaya don ayyukan raya ƙasa da al’umma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kaso 95 cikin 100 na jihar Kaduna ‘yan APC ne – Uba Sani

Jam’iyyar APC a jihar Kaduna ta karɓi sabbin mambobi, ciki har da ’yan majalisar wakilai guda biyar da kuma ’yan majalisar dokokin jihar Kaduna huɗu...

Akwai bukatar Akpabio da Abbas su yi bayanin yadda aka kashe fiye da naira biliyan 18 a ginin ofishin hukumar majalisar dokokin Nijeriya –...

Kungiyar kare haƙƙin jama’a da tabbatar da shugabanci na gaskiya a Nijeriya SERAP ta nemi shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio da kakakin majalisar wakilai Tajudeen...

Mafi Shahara