DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wata fashewa ce da ta biyo baya ta kashe mutane a Sokoto ba harin jirgin sama ba – Hedkwatar tsaron Nijeriya

-

Hedikwatar tsaron Nijeriya ta alakanta mutuwar mutane 10 a jihar Sokoto bayan wani harin jirgin sojin sama da wata fashewa da ta biyo baya.
Kwana biyu da suka wuce, gwamnatin jihar Sokoto ta ce mutum 10 sun mutu yayinda wasu da dama su ka jikkata a wasu kauyukka a karamar hukumar Silame bayan harin da jirgin saman sojoji ya kai wa mutanen bisa kuskure.
Sai dai a sanarwar da ya fitar, daraktan yada labarai na hedkwatar tsaro Manjo Janar Edward Buba, ya ce mace mace da jikkatar da aka samu ba saboda farmakin soji ne kai tsaye ba, wata fashewa ce da ta biyo baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Atiku ya soki gwamnatin Tinubu kan zargin kin bin umurnin kotun koli na ba kananan hukumomi kudadensu kai tsaye

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar, ya bayyana damuwarsa kan yadda gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke jinkirta aiwatar da hukuncin Kotun Koli da...

‘Yan sanda sun cafke wata daliba ‘yar Nijeriya da ta boye hodar iblis a cikin biredi a Indiya

Masu binciken manyan laifuka (Central Crime Branch) a ƙasar Indiya sun cafke wata ’yar Nijeriya mai shekara 29, Olajide Esther Iyanuoluwa, bisa zargin safarar hodar...

Mafi Shahara