DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan jihar Zamfara Dauda ya ba ma’aikatan jihar ‘bonus’ don saukaka musu rayuwa

-

Gwamnatin jihar Zamfara ta amince da ba ma’aikatan gwamnati a jihar kaso 30% na albashinsu a matsayin wani ‘hasahi’ da zai rage musu radadin rayuwa.
A wata sanarwa daga shugaban ma’aikatan gwamnatin jihar Ahmad Aliyu Liman, ta ce karimcin bai tsaya ga ma’aikatan gwamnati kadai ba, hada ‘yan fansho da suka yi ritaya daga aiki.
Sanarwar ta ce wannan karimcin na daga cikin yunkurin gwamnatin jihar na inganta rayuwar ma’aikata da sauran daukacin al’ummar jihar.
Gwamna Dauda Lawan ya bukaci ma’aikatan jihar da su mayar da biki ta hanyar jajircewa wajen aiki don gina jihar ta zarta tsara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Jam’iyyar ADC ta fara rajista da tantance mambobi na kwanaki 90 a fadin Nijeriya

Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta fara shirin rajista, tantancewa da kuma jawo sabbin mambobi na tsawon kwanaki 90 a fadin Nijeriya, domin karfafa jam’iyyar...

Ya kamata a haramta amfani da kafafen sada zumunta ga ’yan kasa da shekara 16 a Nijeriya – Femi Falana

Babban lauya kuma SAN, Femi Falana, ya bukaci a haramta amfani da kafafen sada zumunta ga yara ’yan kasa da shekara 16 a Nijeriya, yana...

Mafi Shahara