DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan jihar Zamfara Dauda ya ba ma’aikatan jihar ‘bonus’ don saukaka musu rayuwa

-

Gwamnatin jihar Zamfara ta amince da ba ma’aikatan gwamnati a jihar kaso 30% na albashinsu a matsayin wani ‘hasahi’ da zai rage musu radadin rayuwa.
A wata sanarwa daga shugaban ma’aikatan gwamnatin jihar Ahmad Aliyu Liman, ta ce karimcin bai tsaya ga ma’aikatan gwamnati kadai ba, hada ‘yan fansho da suka yi ritaya daga aiki.
Sanarwar ta ce wannan karimcin na daga cikin yunkurin gwamnatin jihar na inganta rayuwar ma’aikata da sauran daukacin al’ummar jihar.
Gwamna Dauda Lawan ya bukaci ma’aikatan jihar da su mayar da biki ta hanyar jajircewa wajen aiki don gina jihar ta zarta tsara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Wike ya musanta jita-jitar tsayawarsa takarar shugabancin Nijeriya a zaben 2027, ya jaddada goyon bayansa ga Tinubu har zuwa 2031

Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya karyata rahotannin da ke cewa wasu jiga-jigan jam’iyyar PDP na matsa masa lamba domin ya tsaya takarar shugaban ƙasa a...

Sau 22 ana yunkurin lalata mana matatar mai – Matatar man fetur ta Dangote

Kamfanin matatar mai ta Dangote ya bayyana cewa tun bayan da matatar man da ke fitar da ganga 650,000 a rana ta fara aiki, aƙalla...

Mafi Shahara