Babu rashin jituwa tsakanin mu da gwamnoni kan cin gashin kan kananan hukumomi –Shugaba Tinubu

-

 

Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmad Tinubu ya yi kira da gwamnatocin jihohi da su hada gwiwa domin tunkarar kalubalen da ke addabar kananan hukumomi a kasar.

Shugaba Tinubu ya yi wannan kiran ne a yayin bikin sabuwar shekara tare da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima da wasu gwamnonin Nijeriya da suka yi a gidansa da ke Legas ranar Laraba.

Da yake bayyana kudirinsa na ci gaban kananan hukumomi, a cikin wata sanarwa da mai taimaka wa shugaban kasar kan harkokin yada labarai, Bayo Onanuga ya fitar, ya jaddada muhimmancin ‘yan cin gashin kai ga kananan hukumomi wajen ci gaban kasa da tare da kawar da rade radin rashin jituwa tsakanin sa da gwamnonin.

Inda ya ce babu wata matsala a tsakanin su,illa kokarin kawo sauyi mai dorewa ga kasa ta hanyar baiwa kananan hukumomi dama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun ji takaicin ficewar gwamna Sheriff Oborevwori na jihar Delta daga PDP zuwa APC- Umar Damagum

Shugaban ruko na jam’iyyar PDP na ƙasa, Umar Damagum, ya bayyana ficewar Gwamna Sheriff Oborevwori na Jihar Delta, tare da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar zuwa...

Talauci zai karu a Najeriya nan da 2027 – Bankin Duniya

Bankin Duniya ya bayyana cewa yawan mutanen Najeriya da ke fama da talauci zai karu nan da shekarar 2027, duk da kasancewar kasar na daga...

Mafi Shahara