DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan jihar Ribas Similanayi Fubara ya sanya hannu kan kasafin kudin shekarar 2025 naira tiriliyan 1.188 awanni 48 bayan gabatarwa majalisar dokokin jihar

-

 

Gwamnan jihar Ribas Similanayi Fubara

A wannan Alhamis, 2 ga watan Janairu, 2025, Gwamnan Ribas Similanayi Fubara ya sanya hannu kan kasafin kudin 2025 tare da godewa majalisar dokokin jihar karkashin jagorancin Victor Oko-Jumbo bisa yin kyakkyawan aikin cikin awanni 48.

Gwamnan ya tabbatar da cewa majalisar dokokin wadda Oko-Jumbo ke jagoranta ita ce daya tilo da ake da ita a jihar.

Sai dai gwamna Fubara ya bayyana cewa Martins Amaewhule da wasu mambobi 26 da suka sauya sheka daga jam’iyyarsa ta PDP zuwa jam’iyyar APC ba ‘yan majalisa ne ba, duk kuwa da kokarin da suka yi na janye matakin da suka dauka a kwanakin nan.

Gwamna Fubara dai ya shiga takun saka da wasu ‘yan majalisun jihar da ke goyon bayan ministan Abuja Nyesom Wike, wanda daga baya suka bayyana komawar su jam’iyyar APC.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Farashin buhun shinkafar waje mai nauyin 50KG ya koma N58,000 a wasu sassan Nijeriya in ji wani rahoton da majiyar DCL Hausa ta Punch ta wallafa.

Rahoton da kamfanin S&P Global ya fitar ya bayyana cewa farashin buhun shinkafa mai nauyin kilo 50 ya sauka zuwa N58,000 a wasu yankunan Najeriya,...

‘Yan siyasar da ke neman mukamai ba don talakawa suke yi ba – Zargin Bafarawa ga ‘yan siyasar Nijeriya

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya yi zargin cewa an yi wa siyasar adawa kamshin mutuwa a Najeriya. Bafarawa, wanda ya kasance jigo...

Mafi Shahara