DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnonin Nijeriya za su ci gaba da bai wa shugaban kasar goyon baya wajen magance tsaro da ci gaban tattalin arziki-Gwamnan Kwara

-

 

Abdulrahman Abdulrazaq

Google search engine

Shugaban kungiyar gwamnonin Nijeriya gwamnan jihar Kwara, Abdulrahman Abdulrazaq, ya yaba wa manufofin tattalin arziki na shugaba Bola Tinubu dake kara habbaka jihohin kasar.

Abdulrazaq ya bayyana hakan ne a ranar Laraba, yayin bikin sabuwar shekara da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima da mambobin kungiyar gwamnonin Nijeriya suka kai wa shugaban kasar a gidansa da ke da ke Legas.

Gwamnan ya kuma bayyana nasarorin da aka samu a harkar noma a karkashin gwamnatin Tinubu, inda ya bayar da misali da yadda aka samu amfanin noma mai yawa a jihar Jigawa.

Abdulrazaq ya baiwa shugaban tabbacin ci gaba da bayar da goyon baya wajen magance kalubalen tsaro da ci gaban tattalin arziki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3

Wata kotu a Amurka ta yanke wa wani ɗan Najeriya mai zama a San Gabriel Valley, Abiola Femi Quadri, hukuncin ɗaurin shekara 11 da wata...

Natasha ta sake shan alwashin komawa majalisar dattawa a ranar Talata

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, ‘yar Majalisar Dattawa daga jihar Kogi da aka dakatar, ta shigar da ƙara ga Majalisar Dattawa tana neman su girmama hukuncin Babbar...

Mafi Shahara