DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnonin Nijeriya za su ci gaba da bai wa shugaban kasar goyon baya wajen magance tsaro da ci gaban tattalin arziki-Gwamnan Kwara

-

 

Abdulrahman Abdulrazaq

Shugaban kungiyar gwamnonin Nijeriya gwamnan jihar Kwara, Abdulrahman Abdulrazaq, ya yaba wa manufofin tattalin arziki na shugaba Bola Tinubu dake kara habbaka jihohin kasar.

Abdulrazaq ya bayyana hakan ne a ranar Laraba, yayin bikin sabuwar shekara da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima da mambobin kungiyar gwamnonin Nijeriya suka kai wa shugaban kasar a gidansa da ke da ke Legas.

Gwamnan ya kuma bayyana nasarorin da aka samu a harkar noma a karkashin gwamnatin Tinubu, inda ya bayar da misali da yadda aka samu amfanin noma mai yawa a jihar Jigawa.

Abdulrazaq ya baiwa shugaban tabbacin ci gaba da bayar da goyon baya wajen magance kalubalen tsaro da ci gaban tattalin arziki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 kudin ritayarsu

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya kudin fanshon fiye da Naira biliyan 15 ga tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 Wadanda abin ya...

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da ‘ya’yanta ke yi

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da 'ya'yanta ke yi nan da makon gobe Kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyyar PDP tare da kungiyar gwamnonin...

Mafi Shahara