DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ma’aikatan CBN 1000 da su ka bar aiki ba tursasa su aka yi ba – Gwamnan babban bankin Nijeriya

-

Babban bankin Nijeriya ya yi karin haske cewa, ma’aikata 1000 da su ka bar aiki a shekarar 2024 ba tursasa su aka yi ba don su ajiye aiki.
Gwamnan CBN Olayemi Cardoso, ya sanar da hakan a gaban kwamitin bincike na majalisar wakilai da ke bincike akan dalilin barin aikin ma’aikatan da kuma yadda aka amince da biyansu naira biliyan 50 a matsayin hakkinsu na barin aiki.
Cardoso ya ce duk wadanda abin ya shafa sun ajiye aiki ne bisa radin kansu, karkashin wani shiri na biyan ma’aikata duk hakkokinsu idan su ka ajiye aiki da wuri.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An kaddamar da kafar yaɗa labarai ta Hausa don mata zalla a Nijeriya

An kaddamar da Mata Media, kafar yaɗa labarai ta farko a Nijeriya da aka ware musamman domin mata, wacce ke aikin shirya labarai na abubuwan...

Ku daina nada baragurbin ‘yan siyasa a shugabacin Jami’o’i – Jega ga Tinubu

Tsohon shugaban hukumar zaben Nijeriya INEC, Farfesa Attahiru Jega, ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta daina nada ’yan siyasa marasa kwarewa da mutanen...

Mafi Shahara