DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ma’aikatan CBN 1000 da su ka bar aiki ba tursasa su aka yi ba – Gwamnan babban bankin Nijeriya

-

Babban bankin Nijeriya ya yi karin haske cewa, ma’aikata 1000 da su ka bar aiki a shekarar 2024 ba tursasa su aka yi ba don su ajiye aiki.
Gwamnan CBN Olayemi Cardoso, ya sanar da hakan a gaban kwamitin bincike na majalisar wakilai da ke bincike akan dalilin barin aikin ma’aikatan da kuma yadda aka amince da biyansu naira biliyan 50 a matsayin hakkinsu na barin aiki.
Cardoso ya ce duk wadanda abin ya shafa sun ajiye aiki ne bisa radin kansu, karkashin wani shiri na biyan ma’aikata duk hakkokinsu idan su ka ajiye aiki da wuri.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saki ‘Yan jaridar Sahara FM da aka tsare a Agadez

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na nuna cewa an saki ‘yan jarida uku na gidan rediyon Sahara FM da ke Agadez bayan da aka tsare su...

Kwamishinan Jigawa ya mayar da rarar Naira miliyan 301 daga kudaden da aka ware don shirin ciyar da al’umma a watan Ramadan

Kwamishinan ayyuka na musamman na jihar Jigawa, Alhaji Auwalu Danladi Sankara, ya mayar da Naira miliyan 301 zuwa baitul malin jihar, daga cikin Naira biliyan...

Mafi Shahara