DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad ya yi kira ga shugaba Tinubu ya dubi halin da ‘yan Nijeriya ke ciki domin al’ummar kasar na shan wahala

-

 

Gwamnan jihar Bauchi Bala Muhammad

Gwamnan jihar Bauchi ya yi kira ga shugaba Bola Tinubu da ya saurari halin da ‘yan Nijeriya ke ciki, da ya ce manufofinsa ba sa aiki kuma mutane suna shan wahala.

Da yake jawabi a lokacin da ya karbi bakuncin malaman addinin musulunci karkashin jagorancin Sheikh Sani Yahaya Jingir, gwamnan ya shawarci shugaban kasa da ya saurari ‘yan kasar ya  kuma gyara kura kurai da ya yi.

Ya ce ya zama wajibi shugabanni su gaya wa kansu gaskiya yana fadar hakanne domin shugaban kasa ya gyara kuskurensa domin ’yan kasar suna shan wahala da  su kansu gwamnoni  suna shan wahala saboda tsauraran  manufofin shugaban.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwamishinan Jigawa ya mayar da rarar Naira miliyan 301 daga kudaden da aka ware don shirin ciyar da al’umma a watan Ramadan

Kwamishinan ayyuka na musamman na jihar Jigawa, Alhaji Auwalu Danladi Sankara, ya mayar da Naira miliyan 301 zuwa baitul malin jihar, daga cikin Naira biliyan...

Gwamnatin mulkin sojin Nijar ta karɓi wasikun kulla kawance daga sabbin jakadun ƙasashe 8

A ranar Juma’a, 9 ga Mayu, 2025, fadar gwamatin ta Jamhuriyar Nijar ta karɓi sabbin jakadun daga jakadun ƙasashen duniya guda takwas. Inda shugaban mulkin sojin...

Mafi Shahara