DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaban Bola Tinubu ya sauka abirnin Abu Dhabi na kasar Dubai domin halartar taro

-

 

Shugaba Tinubu

Google search engine

Zuwan shugaba Tinubu zuwa Dubai na zuwa ne bisa gayyatar shugaban kasar, Sheikh Mohamed bin Zayed Al Nahyan.

Mataimaki na musamman ga shugaban Tinubu kan kafafen sadarwa na zamani, Dada Olusegun, ya sanar da hakan Tinubu a shafin sa na X.

Shugaba Bola Tinubu ya gana da karamin ministan harkokin wajen kasar, Sheikh Shakhboot Nahyan Al Nahyan, a lokacin da ya sauka a birnin Abu Dhabi a ranar 12 ga watan Junairu, 2025. A Abu Dhabi.

Ana sa ran shugaban zai gabatar da jawabin da zai bayyana sauye sauyen da gwamnatinsa ta kawo ga Nijeriya, musamman inganta harkokin sufuri, lafiyar al’umma, da ci gaban tattalin arziki.

A yayin ziyarar, Tinubu da tawagarsa za su tattauna da shugabannin kasar don karfafa alakar da ke tsakanin kasashen biyu da kuma lalubo damammaki na huldar tattalin arziki da diflomasiyya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hukumar Tarayyar Turai ta yi Allah-wadai da haramta biza da Amurka ta yi wa wasu Turawa

Tarayyar Turai, tare da ƙasashen Faransa da Jamus, sun yi kakkausar suka ga matakin Amurka na haramta biza ga wasu ’yan Turai da ke yaki...

Shugaba Tinubu ya yi kira ga hadin kai da hakuri a tsakanin addinai a cikin sakon taya murnar bikin Kirsimeti

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su rungumi haɗin kai, juriya da zaman lafiya tsakanin mabiya addinai, yana mai cewa...

Mafi Shahara