DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babban Hafsan Sojin kasa COAS, Olufemi Oluyede, ya amince da canjawa manyan hafsoshi a Nijeriya wajen aiyyu

-

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar, Onyema Nwachukwu, ya fitar ranar Asabar a Abuja.

Nwachukwu, ya bayyana cewa, sake tura sojoji wani shiri ne na inganta aiki ayyukan rundunar.

Ya ce jami’an da abin ya shafa sun hada da kwamandojin rundunar, manyan hafsoshi, manyan kwamandojin (GOC), kwamandojin cibiyoyin horar da sojoji, birgediya da sauran manyan mukamai.

 A cewarsa, sake tura dakarun da kuma sauyawa wasu wuraren aiki na nuni da kudurin rundunar na tabbatar da tsarin jagoranci da zai iya magance matsalolin tsaro a fadin kasar.

Mista Nwachukwu ya ce wasu daga cikin manyan hafsoshin da aka canza wa wajen a hedkwatar sojojin sun hada da Manjo Janar Lawrence Fejokwu, daga Kwalejin Tsaro ta kasa zuwa sashin kula da harkokin soji, wanda aka nada shi Shugaban Gudanarwa na rundunar Soji.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Farashin buhun shinkafar waje mai nauyin 50KG ya koma N58,000 a wasu sassan Nijeriya in ji wani rahoton da majiyar DCL Hausa ta Punch ta wallafa.

Rahoton da kamfanin S&P Global ya fitar ya bayyana cewa farashin buhun shinkafa mai nauyin kilo 50 ya sauka zuwa N58,000 a wasu yankunan Najeriya,...

‘Yan siyasar da ke neman mukamai ba don talakawa suke yi ba – Zargin Bafarawa ga ‘yan siyasar Nijeriya

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya yi zargin cewa an yi wa siyasar adawa kamshin mutuwa a Najeriya. Bafarawa, wanda ya kasance jigo...

Mafi Shahara