DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumar kula da shige da fice “Immigration” ta tseratar da mutanen da aka yi yunkurin safararsu a Jigawa

-

Hukumar lura da shige da fice ta Najeriya Immigration a jihar Jigawa ta kubutar da mutum 10 da ake zargin an yi safarar su ya yin wani samame da ta kai a karamar hukumar Babura.
Shugaban hukumar a jihar CIS Musa ne , ya bayyana haka a lokacin da yake ganawa da manema Labarai a ofishin sa dake birnin Dutse.
Ya ce bayan samamen da aka kai mai taken ‘Operation Salama’ a Naira Tsamiyar Kwance a Babura, an kubutar da Mata 8 sai Maza biyu da ke kan hanyar zuwa Turai.
CIS Musa, ya ce wadan da aka yi safarar su matasa ne da shekarun su ke tsakanin 21 zuwa 30, kuma sun fito ne daga jihohin Ogun sai Oyo da Ondo da kuma Imo.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara