DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sojoji na bukatar kayan aiki na zamani don yakar ‘yan bindiga da masu aikata manyan laifuka – Matawalle

-

Ministan kasa a ma’aikatar tsaron Nijeriya/Bello Muhammad Matawalle

 

Ministan kasa a ma’aikatar tsaron Nijeriya, Bello Matawalle, ya bukaci a kara hada kai da samar da kudade ga bangaren tsaro domin yakar ‘yan bindiga da sauran miyagun laifuka a fadin kasar kasar.

Google search engine

Matawalle ya yi wannan roko ne a yayin kare kasafin kudin shekarar 2025 na ma’aikatar tsaro ga kwamitocin tsaro na majalisar dattawa da ta wakilai a Abuja.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da daraktan yada labarai na ma’aikatar tsaro, Daberechi Asonye, ​​ ranar Alhamis a Abuja.

Ministan ya jaddada muhimmancin hadin gwiwa  da ‘yan majalisar, inda ya kara da cewa duka kwamitocin majalisar da na dattawa sun nuna jajircewa da hadin kai domin tabbatar da ma’aikatar tsaro ta samu abinda take bukatawa don ganin an kori ‘yan bindiga da sauran bata gari.

Ya ce wgoyon bayan da suka ba su ya taimaka matuka wajen nasarorin da ma’aikatar ta samu zuwa yanzu. Sai dai ya ce akwai bukatar samun sabbin kayan aiki domin ci gaba da tunkarar kalubalen tsaro a kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin Nijar ta kaddamar da sabon ofishin kamfanin shinkafar gida

Ministan kasuwancin jamhuriyar Nijar, Malam Abdoulaye Seydou ya jagoranci kaddamar da sabon ofishin kamfanin shinkafar gida a babban birnin Yamai a ranar Litinin 13 ga...

Gwamnatin Nijeriya za ta dauki mataki kan barnar kudaden shiga a bangaren hakar ma’adanai

Ministan ma’adanai, Dele Alake, ya bayyana cewa gwamnatin Nijeriya na shirin kafa sabuwar hukuma da za ta rika sa ido kan fitar da ma’adanai kafin...

Mafi Shahara