DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sojoji na bukatar kayan aiki na zamani don yakar ‘yan bindiga da masu aikata manyan laifuka – Matawalle

-

Ministan kasa a ma’aikatar tsaron Nijeriya/Bello Muhammad Matawalle

 

Ministan kasa a ma’aikatar tsaron Nijeriya, Bello Matawalle, ya bukaci a kara hada kai da samar da kudade ga bangaren tsaro domin yakar ‘yan bindiga da sauran miyagun laifuka a fadin kasar kasar.

Google search engine

Matawalle ya yi wannan roko ne a yayin kare kasafin kudin shekarar 2025 na ma’aikatar tsaro ga kwamitocin tsaro na majalisar dattawa da ta wakilai a Abuja.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da daraktan yada labarai na ma’aikatar tsaro, Daberechi Asonye, ​​ ranar Alhamis a Abuja.

Ministan ya jaddada muhimmancin hadin gwiwa  da ‘yan majalisar, inda ya kara da cewa duka kwamitocin majalisar da na dattawa sun nuna jajircewa da hadin kai domin tabbatar da ma’aikatar tsaro ta samu abinda take bukatawa don ganin an kori ‘yan bindiga da sauran bata gari.

Ya ce wgoyon bayan da suka ba su ya taimaka matuka wajen nasarorin da ma’aikatar ta samu zuwa yanzu. Sai dai ya ce akwai bukatar samun sabbin kayan aiki domin ci gaba da tunkarar kalubalen tsaro a kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3

Wata kotu a Amurka ta yanke wa wani ɗan Najeriya mai zama a San Gabriel Valley, Abiola Femi Quadri, hukuncin ɗaurin shekara 11 da wata...

Natasha ta sake shan alwashin komawa majalisar dattawa a ranar Talata

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, ‘yar Majalisar Dattawa daga jihar Kogi da aka dakatar, ta shigar da ƙara ga Majalisar Dattawa tana neman su girmama hukuncin Babbar...

Mafi Shahara