DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Al-Hilal ba za ta yi wa Neymar Jnr rijista ba

-

Kungiyar kwallon kafa ta Al Hilal dake kasar Saudi Arabia, ba zata yi wa gwarzon dan wasan kasar Brazil Neymar Junior rijistar buga zagaye na biyu na gasar kakar wasannin firimiyar kasar ba ta 2025.

Hakan ya biyo bayan nazarin lafiyar dan wasan da tawagar ta yi na irin gudunmowar da zai bawa kungiyar.
A baya Neymar ya samu zunzurutun kudi Euro Miliyan 101 a shekarar 2024, a wasanni biyu kacal da ya shafe mintuna 42 a cikin filin wasa.
Ya shafe tsawon watanni 6, ya na fama da jinyar rauni abinda ya sa a yanzu haka Al Hilal ke dari -darin tsawaita kwantiragin sa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tankiya tsakanin Nijer da Benin ta sa kasashen rufe ofisoshin jakadancin juna

Kasashen Benin da Niger sun kori jami’an diflomasiyyar juna a wani mataki na ramuwar gayya, bayan shafe kusan shekara biyu ana takun-saka a tsakaninsu, a...

‘Yan bindiga sun yi ajalin mutane fiye da 30 a jihar Neja

Aƙalla mutane 30, ciki har da mata, sun rasu bayan da ‘yan bindiga suka kai hari Kasuwan Daji da ke ƙauyen Demo, Borgu LGA a...

Mafi Shahara