DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Mahajjata daga Nijeriya za su biya Naira milyan 8.4 kudin aikin hajji a shekarar 2025

-

 

Hakan na kunshe a cikin wata sanarwa da mataimakiyar daraktan yada labaran hukumar Fatima Sanda Usara ta fitar a ranar Litinin. 

Google search engine

Sanarwar ta ce hukumar karkashin jagorancin shugabanta Farfesa Abdullahi Sale Usman tare da manyan sakatarorinta da masu ruwa da tsaki sun cimma matsaya bisa duba na tsanaki kan kudin da kowane Alhajin Nijeriya zai biya a shekarar 2025.

A cewar sanarwar mahajjatan da suka fito daga shiyyar Borno da Adamawa,za su biya Naira miliyan 8.3.Hakazalika, maniyyatan da suka fito daga jihohin Kudu za su biya Naira miliyan 8.7.

Sai kuma alhazan da suka fito daga yankin Arewa za su biya Naira miliyan 8.4.

Shugaban hukumar Farfesa Saleh ya bukaci mahajjatan da suke son zuwa aikin Hajji da su bi dukkan ka’idojin kasar Saudiyya ta gindaya tare da jaddada muhimmancin biyan kudi da wuri da kuma yin rajista a kan lokaci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnonin da suka sha suka ta yanzu sun koma jam’iyyar APC – Ministan Abuja Wike

Ministan birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya ce ficewar wasu gwamnonin jam’iyyar adawa ta PDP zuwa jam’iyyar APC ta tabbatar da goyon bayansa ga Shugaba...

Majalisar Dattawan Nijeriya za ta tantance sabon shugaban INEC ranar Alhamis

Majalisar Dattawan Nijeriya ta shirya tantance Farfesa Joash Amupitan, wanda shugaba Bola Ahmed Tinubu ya zaba domin zama sabon shugaban hukumar zaben Nijeriya INEC, a...

Mafi Shahara