DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan Nijeriya milyan 70 za su amfana da tallafin kudi Naira 75,000 kowanensu don rage radadin fatara

-

Shugaba Bola Tinubu

 

Gwamnatin Nijeriya ta kammala shirye shiryen raba tsabar kudi Naira 75,000 ga ‘yan kasar miliyan 70 a wani yunkuri na rage radadin fatara.

Google search engine

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi babban mataimaki na musamman ga shugaban kasar kan harkokin al’umma, Hon. Aliyu Audu,ya bayyana cewa matakin ya dace da kudurin gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu na yakar talauci a fadin kasar.

Audu, wanda kuma shi ne shugaban kungiyar masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC, ya bayyana cewa hakan ya tabbatar da shugaba Tinubu ya nuna kwazo a cikin watanni 19 kacal da ya yi yana mulkar kasar

Ya kara da cewa jajircewar manufofin Tinubu sun samar da sakamako mai kyau, wanda hakan yasa ake ci gaba da samun masu zuba hannun jari zuwa kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Ni ne dan siyasa na biyu da aka fi ci wa zarafi a Nijeriya – Nyesom Wike

Ministan Abuja Nyesom Wike ya bayyana cewa shi ne dan siyasa na biyu da aka fi ci wa zarafi a Nijeriya bayan shugaban kasa Bola...

Kwankwaso ya umurci a ba ’ya’yan ’yan majalisar Kano da suka rasu tikitin takarar maye gurbinsu

Jagoran darikar Kwankwasiyya Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso, ya umarci a bai wa 'ya'yan 'yan majalisar dokokin jihar Kano guda biyu da suka rasu damar tsayawa...

Mafi Shahara