DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan Nijeriya milyan 70 za su amfana da tallafin kudi Naira 75,000 kowanensu don rage radadin fatara

-

Shugaba Bola Tinubu

 

Gwamnatin Nijeriya ta kammala shirye shiryen raba tsabar kudi Naira 75,000 ga ‘yan kasar miliyan 70 a wani yunkuri na rage radadin fatara.

Google search engine

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi babban mataimaki na musamman ga shugaban kasar kan harkokin al’umma, Hon. Aliyu Audu,ya bayyana cewa matakin ya dace da kudurin gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu na yakar talauci a fadin kasar.

Audu, wanda kuma shi ne shugaban kungiyar masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC, ya bayyana cewa hakan ya tabbatar da shugaba Tinubu ya nuna kwazo a cikin watanni 19 kacal da ya yi yana mulkar kasar

Ya kara da cewa jajircewar manufofin Tinubu sun samar da sakamako mai kyau, wanda hakan yasa ake ci gaba da samun masu zuba hannun jari zuwa kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnan Kano ya rattaba hannu kan bukatar samar da kwalejin Polytechnic a Gaya

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan dokar kafa kwalejin kimiyya da fasaha "Gaya Polytechnic" a wani mataki na fadada damar samun ilimin...

Ma’aikatan majalisa sun rufe majalisar dokokin jihar Bauchi sakamakon tsunduma yajin aiki 

Shugaban ƙungiyar ma’aikatan majalisun jihohi ta Nijeriya (PASAN) a jihar Bauchi Adamu Yusuf ne ya sanar da hakan ranar Juma’a, bisa bin umarnin shugabancin ƙungiyar...

Mafi Shahara