DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan Nijeriya milyan 70 za su amfana da tallafin kudi Naira 75,000 kowanensu don rage radadin fatara

-

Shugaba Bola Tinubu

 

Gwamnatin Nijeriya ta kammala shirye shiryen raba tsabar kudi Naira 75,000 ga ‘yan kasar miliyan 70 a wani yunkuri na rage radadin fatara.

Google search engine

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi babban mataimaki na musamman ga shugaban kasar kan harkokin al’umma, Hon. Aliyu Audu,ya bayyana cewa matakin ya dace da kudurin gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu na yakar talauci a fadin kasar.

Audu, wanda kuma shi ne shugaban kungiyar masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC, ya bayyana cewa hakan ya tabbatar da shugaba Tinubu ya nuna kwazo a cikin watanni 19 kacal da ya yi yana mulkar kasar

Ya kara da cewa jajircewar manufofin Tinubu sun samar da sakamako mai kyau, wanda hakan yasa ake ci gaba da samun masu zuba hannun jari zuwa kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Jam’iyyar PDP a Jigawa ta soki dakatar da Sule Lamido, daga kwamitin amintattu na jam’iyyar

Jam’iyyar PDP reshen jihar Jigawa ta nuna rashin jin daɗi kan matakin dakatar da Sule Lamido, CON, daga ayyukan kwamitin amintattu na jam’iyyar,tana mai kira...

Gasar cin kofin kasashen nahiyar Afirka AFCON za ta koma duk bayan shekaru 4 – CAF

Hukumar kwallon kafa ta nahiyar Afrika CAF, ta sanar da cewa gasar cin kofin kasashen Afrika AFCON, za ta koma duk bayan shekara huɗu bayan...

Mafi Shahara