DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hadakar kungiyoyin Arewacin Nijeriya CNG ta yi Allah wadai da amincewar da Hukumar sadarwa ta kasar NCC ta yi wa kamfanonin sadarwa na karin kashi 50% na kudin kira da na data a kasar

-

 

CNG

A wani bayani da Kodinetan kungiyar na kasa Kwamared Jamilu Aliyu Charanchi ya fitar, yace wannan matakin zai ƙara jefa al’umma cikin halin matsin rayuwa da suke ciki.

Google search engine

Kungiyar ta nanata cewa kalaman gwamnati na tuntubar masu ruwa da tsaki shaci-faɗi ne domin ‘yan Nijeriya dake shan wahalar saka kudin sadarwa ba su cikin wannan tuntubar.

Da wannan ƙarin da aka yi, kudin kira za su tashi daga  N11 zuwa N16.50 duk minti ɗaya, inda tura sako zai kai N6 daga Naira 4, hakama kudin data zai tashi daga N350 zuwa N431.25 akan kowace 1gb.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An kaddamar da kafar yaɗa labarai ta Hausa don mata zalla a Nijeriya

An kaddamar da Mata Media, kafar yaɗa labarai ta farko a Nijeriya da aka ware musamman domin mata, wacce ke aikin shirya labarai na abubuwan...

Ku daina nada baragurbin ‘yan siyasa a shugabacin Jami’o’i – Jega ga Tinubu

Tsohon shugaban hukumar zaben Nijeriya INEC, Farfesa Attahiru Jega, ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta daina nada ’yan siyasa marasa kwarewa da mutanen...

Mafi Shahara