DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hadakar kungiyoyin Arewacin Nijeriya CNG ta yi Allah wadai da amincewar da Hukumar sadarwa ta kasar NCC ta yi wa kamfanonin sadarwa na karin kashi 50% na kudin kira da na data a kasar

-

 

CNG

A wani bayani da Kodinetan kungiyar na kasa Kwamared Jamilu Aliyu Charanchi ya fitar, yace wannan matakin zai ƙara jefa al’umma cikin halin matsin rayuwa da suke ciki.

Google search engine

Kungiyar ta nanata cewa kalaman gwamnati na tuntubar masu ruwa da tsaki shaci-faɗi ne domin ‘yan Nijeriya dake shan wahalar saka kudin sadarwa ba su cikin wannan tuntubar.

Da wannan ƙarin da aka yi, kudin kira za su tashi daga  N11 zuwa N16.50 duk minti ɗaya, inda tura sako zai kai N6 daga Naira 4, hakama kudin data zai tashi daga N350 zuwa N431.25 akan kowace 1gb.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan sanda sun kama mutumin da ake zargi da aikata assha da diyarsa a jihar Bauchi

Rundunar ’yan sandan jihar Bauchi ta kama wani mutum mai shekaru 28 bisa zargin lalata da ’yarsa ta cikinsa ’yar shekara takwas, lamarin da ya...

Shugaba Tinubu na hasashen samun saukin hauhawar farashi a Nijeriya cikin 2026

Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya yi hasashen cewa hauhawar farashin kayayyaki a kasar zai sauka kasa da kashi 10 cikin 100 a shekarar 2026,...

Mafi Shahara