DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hadakar kungiyoyin Arewacin Nijeriya CNG ta yi Allah wadai da amincewar da Hukumar sadarwa ta kasar NCC ta yi wa kamfanonin sadarwa na karin kashi 50% na kudin kira da na data a kasar

-

 

CNG

A wani bayani da Kodinetan kungiyar na kasa Kwamared Jamilu Aliyu Charanchi ya fitar, yace wannan matakin zai ƙara jefa al’umma cikin halin matsin rayuwa da suke ciki.

Kungiyar ta nanata cewa kalaman gwamnati na tuntubar masu ruwa da tsaki shaci-faɗi ne domin ‘yan Nijeriya dake shan wahalar saka kudin sadarwa ba su cikin wannan tuntubar.

Da wannan ƙarin da aka yi, kudin kira za su tashi daga  N11 zuwa N16.50 duk minti ɗaya, inda tura sako zai kai N6 daga Naira 4, hakama kudin data zai tashi daga N350 zuwa N431.25 akan kowace 1gb.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Farashin buhun shinkafar waje mai nauyin 50KG ya koma N58,000 a wasu sassan Nijeriya in ji wani rahoton da majiyar DCL Hausa ta Punch ta wallafa.

Rahoton da kamfanin S&P Global ya fitar ya bayyana cewa farashin buhun shinkafa mai nauyin kilo 50 ya sauka zuwa N58,000 a wasu yankunan Najeriya,...

‘Yan siyasar da ke neman mukamai ba don talakawa suke yi ba – Zargin Bafarawa ga ‘yan siyasar Nijeriya

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya yi zargin cewa an yi wa siyasar adawa kamshin mutuwa a Najeriya. Bafarawa, wanda ya kasance jigo...

Mafi Shahara