DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tsohon shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya yi kira ga shugabanni a kowane mataki na gwamnati da su rika tabbatar da gaskiya da rikon amana ga wadanda suke shugabanta

-

 

Muhammad Buhari

Google search engine

Buhari ya bayyana haka ne a dakin taro na Banquet Hall da ke fadar gwamnatin jihar Katsina, a yayin taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC gabanin zaben kananan hukumomin jihar a ranar 15 ga watan Fabrairu.

Tsohon shugaban kasar ya ce wadannan abubuwa na da matukar mahimmanci wajen samun daidaito a tsakanin al’umma da shugabanni da ke jagorantar su a dukkan matakai.

A nasa bangaren, Gwamna Dikko Radda, ya ce jihar ta kuduri aniyar gudanar da zabe na gaskiya, sai dai gwamnan ya umurci masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC a jihar da su hada kai don tabbatar da nasarar jam’iyyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hukumar Tarayyar Turai ta yi Allah-wadai da haramta biza da Amurka ta yi wa wasu Turawa

Tarayyar Turai, tare da ƙasashen Faransa da Jamus, sun yi kakkausar suka ga matakin Amurka na haramta biza ga wasu ’yan Turai da ke yaki...

Shugaba Tinubu ya yi kira ga hadin kai da hakuri a tsakanin addinai a cikin sakon taya murnar bikin Kirsimeti

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su rungumi haɗin kai, juriya da zaman lafiya tsakanin mabiya addinai, yana mai cewa...

Mafi Shahara