DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wata tankin mai ta sake fashewa a titin Engu-Onitsha, ta yi ajalin mutane 11

-

 

Google search engine

Akalla mutane 11 ne suka mutu sakamakon fashewar wata tankar mai dauke da man fetur a hanyar Enugu zuwa Onitsha a ranar Asabar.

A lokacin da tankar man ta fadi ta zubar da man da ke cikinta, kafin ta fashe.

Da yake jawabi kan faruwar lamarin, Gwamnan jihar Peter Mbah ya ce wadanda suka jikkata na samun kulawar likitoci, kuma jihar za ta dauki matakin dakile afkuwar lamarin nan gaba da suka hada da tabbatar da dokar hanya da kuma gyaran hanyar gwamnatin tarayya da ta lalace.

Mbah ya jajantawa iyalan wadanda suka mutu da wadanda suka jikkata a yayin afkuwar lamarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hukumar Tarayyar Turai ta yi Allah-wadai da haramta biza da Amurka ta yi wa wasu Turawa

Tarayyar Turai, tare da ƙasashen Faransa da Jamus, sun yi kakkausar suka ga matakin Amurka na haramta biza ga wasu ’yan Turai da ke yaki...

Shugaba Tinubu ya yi kira ga hadin kai da hakuri a tsakanin addinai a cikin sakon taya murnar bikin Kirsimeti

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su rungumi haɗin kai, juriya da zaman lafiya tsakanin mabiya addinai, yana mai cewa...

Mafi Shahara