DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin tarayya ta bai wa iyalan wanda ya zana tutar Nijeriya tallafin milyan 30

-

 

Shugaba Tinubu

Google search engine

Gwamnatin tarayya ta bayar da gudummawar N30m ga iyalan wanda ya yi zanen tutar Nijeriya, Taiwo Akinkunmi, a ranar Alhamis.

Babban daraktan hukumar wayar da kan jama’a ta kasa Lanre Issa Onilu tare da rakiyar daraktan hukumar na jihar Oyo Olukemi Afolayan ne suka gabatar da cakin kudin a madadin gwamnatin tarayya a fadar gwamnati da ke Elebu, Ibadan, jihar Oyo.

Jaridar PUNCH ta ruwaito cewa Marigayi Akinkunmi ya rasu ne a ranar 29 ga watan Agustan 2023, yana da shekaru 87 a duniya.

A ranar 4 ga Satumba, 2023, Shugaba Bola Tinubu ya aike da wata tawaga karkashin jagorancin ministan yada labarai da wayar da kan jama’a Mohammed Idris, domin yi wa iyalan ta’aziyya, inda gwamnatin ta yi alkawarin tallafa wa iyalan marigayin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Fadar Shugaba Tinubu ta soki Atiku kan kwatanta gwamnatinsa da ta mulkin soja

Fadar Shugaban Nijeriya ta caccaki madugun adawa Atiku Abubakar, bisa kwatanta gwamnatin Tinubu da mulkin soja, tana mai bayyana kalaman nasa a matsayin abinda basu...

Majalisar Dattawa ta dakatar da muhawara kan gyaran dokar zabe tare da shiga zaman sirri

Majalisar Dattawan Nijeriya ta dakatar da muhawarar kan kudirin dokar zaɓe ta 2022, domin bai wa ’yan majalisa damar yin nazari mai zurfi kafin ɗaukar...

Mafi Shahara