DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Tarayya ta ce nan da wasu ‘yan watanni za a kara kudin wutar lantarki a Nijeriya

-

 

Shugaba Tinubu

Google search engine

Mai baiwa shugaba Bola Tinubu shawara na musamman kan harkokin makamashi, Olu Verheijen, ta bayyana haka a taron shugabannin kasashen Afirka kan makamashi da aka yi a Dar es Salaam na kasar Tanzania, inda Nijeriya ta gabatar da wani shiri na dala biliyan 32 da nufin bunkasa wutar lantarki nan da shekarar 2030.

A cewarta Nijeriya na kokarin warware yin wasu sauye sauye masu inganci don jawo hankalin masu zuba jari zuwa kasar musamman ta fuskar makamashi.

Ta ce daya daga cikin manyan kalubalen da ake neman warwarewa a cikin ‘yan watanni masu zuwa shine canza farashin wutar lantarki don ci gaba da samun kudaden shiga.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Buhari mutum ne mai girmama al’adu da masarautu – Sarkin Musulmi

Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, ya shiga sahun wadanda ke jimamin rasuwar tsohon Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari, wanda ya rasu a wani asibiti a...

An rufe ofishin jakadancin Amurka na Abuja da Legas don jimamin rasuwat Buhari

Ofishin jakadancin Amurka da ke Abuja da kuma na Legas za su kasance a rufe a ranar Talata, 15 ga Yuli, 2025, domin girmamawa da...

Mafi Shahara