DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Yaro Yaro ya zama sabon mai horar da Kano Pillars bayan dakatar da Usman Abdullahi

-

 

Yaro Yaro

Google search engine

Tsohon dan wasan tawagar Super Eagles da Borussia Dortmund Ahmed Garba Yaro Yaro ya zama sabon mai horar da kungiyar Kano Pillars.

Hakan ya biyo bayan dakatar da mai horar da kungiyar Usman Abdullah da mahukuntan kungiyar ta Pillars suka yi biyo bayan rashin abun azo gani da kumgiyar ke yi a bana.

Canjaras da kungiyar ta yi da Bayelsa United ya kara harzuka magoya baya dsshugabanni na tawagar sai Masu Gida, da hakan ke biyo bayan dukan kawo wuka na ci 4-1 da ta karba a hannun Ikorodu United ta Lagos a Larabar makon da ya gabata.

A Sanarwar da kungiyar ta fitar ta bakin shugaban tawagar Alhaji Ali Nayara, Yaro Yaro wanda tsohon dan wasan kungiyar ne ta Pillars zai jagoranci kungiyar a yanzu kafin kwamitin bincike da aka kafa kan Usman Abdullah ya kammala aikin sa don samun matsaya a gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Sarkin Musulmi ya bukaci gwamnati da ta yi doka kan amfani da kafafen sada zumunta

Sarkin Musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar III ya bukaci gwamnati da ta yi doka domin daidaita amfani da kafafen sada zumunta a Nijeriya saboda yadda ake...

Jam’iyyar ADC ta zargi shugaba Tinubu da son maida Nijeriya amfani da jam’iyya guda

Jam’iyyar ADC ta zargi shugaba Bola Ahmed Tinubu da ƙoƙarin juya Nijeriya zuwa kasa mai amfani da jam’iyya ɗaya, bayan ficewar wasu gwamnonin jihohi daga...

Mafi Shahara