DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Yaro Yaro ya zama sabon mai horar da Kano Pillars bayan dakatar da Usman Abdullahi

-

 

Yaro Yaro

Google search engine

Tsohon dan wasan tawagar Super Eagles da Borussia Dortmund Ahmed Garba Yaro Yaro ya zama sabon mai horar da kungiyar Kano Pillars.

Hakan ya biyo bayan dakatar da mai horar da kungiyar Usman Abdullah da mahukuntan kungiyar ta Pillars suka yi biyo bayan rashin abun azo gani da kumgiyar ke yi a bana.

Canjaras da kungiyar ta yi da Bayelsa United ya kara harzuka magoya baya dsshugabanni na tawagar sai Masu Gida, da hakan ke biyo bayan dukan kawo wuka na ci 4-1 da ta karba a hannun Ikorodu United ta Lagos a Larabar makon da ya gabata.

A Sanarwar da kungiyar ta fitar ta bakin shugaban tawagar Alhaji Ali Nayara, Yaro Yaro wanda tsohon dan wasan kungiyar ne ta Pillars zai jagoranci kungiyar a yanzu kafin kwamitin bincike da aka kafa kan Usman Abdullah ya kammala aikin sa don samun matsaya a gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dalori ya karbi ragamar jagorancin jam’iyyar APC a hukumance

Shugaban riko na jam’iyyar APC, Ali Bukar Dalori, ya bukaci shugabanni da mambobin jam’iyyar da su zauna cikin hadin kai bayan murabus din tsohon shugaban...

An dakatar da jirgin Rano Air kan zargin matsalar inji – NCAA

Hukumar kula da sufurin jiragen sama ta Najeriya (NCAA) ta dakatar da wani jirgin Rano Air mai lamba 5N-BZY bayan fuskantar hatsarin gobara da matsalar...

Mafi Shahara