DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Nnamdi Kanu ya bukaci kotu tayi watsi da shari’ar da ake yi masa

-

Google search engine

Shugaban haramtacciyar Kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafara(IPOB) Nnamdi Kanu ya nuna bukatar mai sharia’a Binta Nyako da ta kori karar da ke zargin sa a shari’ar da ke gudana tsakanin shi da gwamnati.

A Zaman kotun da ya gudana a babbar kotun tarayya da ke Abuja a safiyar Litinin dinnan Aloy Ejimakor, lauyan Nnamdi Kanu, ya ce bukatar ta sake yin watsi da shari’ar ya fito ne daga wanda yake karewa.

Nnamdi Kanu, wanda ke hannun hukumar tsaro ta farin kaya (SSS) tun shekarar 2021, yana gurfana a gaban Misis Nyako bisa zargin ta’addanci da cin amanar kasa da ke da nasaba da fafutukar neman ballewa daga kasar a matsayin mai fafutukar kafa kasar Biafra.

Ya isa harabar kotun ne tare da jami’an tsaro na DSS da misalin karfe 8:30 na safiyar ranar Litinin

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan bindiga sun hallaka manoma 32 a jihar Niger

Akalla manoma 32 ne aka hallaka a hare-haren da ’yan bindiga suka kai kan al’ummomin Tugan-Makeri, Konsoko da Pissa a karamar hukumar Borgu ta Jihar...

Peter Obi ya bukaci matasa da su nuna kauna da kishin Nijeriya albarkacin ranar masoya

Tsohon ɗan takarar shugaban Nijeriya, Peter Obi, ya bukaci ’yan Nijeriya musamman matasa su yi bikin ranar masoya ta Valentine cikin nuna kishin ƙasa da...

Mafi Shahara