Nnamdi Kanu ya bukaci kotu tayi watsi da shari’ar da ake yi masa

-

Shugaban haramtacciyar Kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafara(IPOB) Nnamdi Kanu ya nuna bukatar mai sharia’a Binta Nyako da ta kori karar da ke zargin sa a shari’ar da ke gudana tsakanin shi da gwamnati.

A Zaman kotun da ya gudana a babbar kotun tarayya da ke Abuja a safiyar Litinin dinnan Aloy Ejimakor, lauyan Nnamdi Kanu, ya ce bukatar ta sake yin watsi da shari’ar ya fito ne daga wanda yake karewa.

Nnamdi Kanu, wanda ke hannun hukumar tsaro ta farin kaya (SSS) tun shekarar 2021, yana gurfana a gaban Misis Nyako bisa zargin ta’addanci da cin amanar kasa da ke da nasaba da fafutukar neman ballewa daga kasar a matsayin mai fafutukar kafa kasar Biafra.

Ya isa harabar kotun ne tare da jami’an tsaro na DSS da misalin karfe 8:30 na safiyar ranar Litinin

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun ji takaicin ficewar gwamna Sheriff Oborevwori na jihar Delta daga PDP zuwa APC- Umar Damagum

Shugaban ruko na jam’iyyar PDP na ƙasa, Umar Damagum, ya bayyana ficewar Gwamna Sheriff Oborevwori na Jihar Delta, tare da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar zuwa...

Talauci zai karu a Najeriya nan da 2027 – Bankin Duniya

Bankin Duniya ya bayyana cewa yawan mutanen Najeriya da ke fama da talauci zai karu nan da shekarar 2027, duk da kasancewar kasar na daga...

Mafi Shahara