DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wata babbar mota tirela da ta kwace ta yi ajalin mutane da dama a Kano

-

Rahotanni sun nuna cewa mutane da dama sun rasu yayin da wasu suka jikkata bayan da wata tirela ta kwace akan gadar Muhammad Buhari da ke Kano kan titin Mariri zuwa Unguwa Uku.
Hatsarin ya faru ne sanadiyar katsewar birkin motar wadda ke kan hanyar zuwa kudancin Nijeriya, kamar yadda jaridar Dailytrust ta ruwaito.
Wani shaidar gani da ido ya ce motar ta kwace ne yayin da direban yake kokarin wucewa kan mararrabar da ke kasan hanyar wadda za ta wuce zuwa titin Ring Road kuma ta hada da babban titin Zaria.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3

Wata kotu a Amurka ta yanke wa wani ɗan Najeriya mai zama a San Gabriel Valley, Abiola Femi Quadri, hukuncin ɗaurin shekara 11 da wata...

Natasha ta sake shan alwashin komawa majalisar dattawa a ranar Talata

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, ‘yar Majalisar Dattawa daga jihar Kogi da aka dakatar, ta shigar da ƙara ga Majalisar Dattawa tana neman su girmama hukuncin Babbar...

Mafi Shahara