HomeUncategorizedSaudiyya ta ba Nijeriya tallafin ton 100 na dabino

Saudiyya ta ba Nijeriya tallafin ton 100 na dabino

-

Dabino

 

Ofishin jakadancin Saudiyya da ke Abuja ya gudanar da wani biki a hukumance don raba tan 100 na dabino ga Nijeriya a wani bangare na ayyukan agaji da take yi duk shekara.

Shirin wanda cibiyar ba da agaji da jinkai ta Sarki Salman (KSrelief) ta dauki nauyin gudanarwa, na da nufin tallafawa iyalai masu karamin karfi a fadin kasar da kuma karfafa dankon zumunci tsakanin kasashen biyu.

A yayin bikin, jakadan a Nijeriya Faisal bin Ibrahim, ya bayyana kwazon masarautar ta Saudiyya kan ayyukan jin kai.

Ya kuma bayyana godiyarsa ga Sarki Salman bin Abdulaziz da Yarima mai jiran gado Mohammed bin Salman bisa goyon bayan da suke ba wa musulmi da al’ummomin da ba a fadin duniya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Sarkin Daura ya nada Hamza Sule Sarautar Sadaukin Kasar Hausa

Maimartaba Sarkin Daura Alh Faruk Umar Faruk ya nada Hon. Hamza Sulaiman Faskari Kwamishinan mahallin jihar katsina sarautar Sadaukin Kasar Hausa a fadarsa dake garin...

Kawance domin kayar da Tinubu a 2027 ba zai yi wani tasiri ba, bata lokaci ne kawai, in ji dan jam’iyyar PDP Ayo Fayose

Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose, ya yi watsi da gamayyar jam’iyyun adawa na siyasa da ake tattaunawa a kai, da nufin kifar da Gwamnatin...

Babu wanda ya hana Kasshim Shettima shiga fadar Shugaban kasa ta Villa, labarin ba ya da tushe bare makama – Mai magana da yawunsa...

Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai Stanley Nkwocha,ya bayyana labarin da ke yawo a kafafan sada zumunta, dangane da hana...

Jiga-jigan APC sun tattaru a Abuja, sun tabbatar wa da Shugaba Tinubu zai yi nasara da gagarumin rinjaye a zaben 2027

Jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki sun gudanar da wani gangami a Abuja, inda suka bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai samu gagarumin rinjaye a...

Most Popular

spot_img