DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Masu garkuwa da mutane sun yi shigar jami’an EFCC tare da yin awon gaba da mutum 10 a Neja

-

Google search engine
Wasu ‘yan bindiga da sojan gonar jami’an hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta Nijeriya EFCC, sun yi garkuwa da mutane 10 a wani otal da ke kan hanyar Shiroro a karamar hukumar Chanchaga a Jihar Neja.
Wani mai lura da harkokin tsaro Zagazola Makama, ya ruwaito wata majiya na cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 4:58 na safiyar ranar Talata, 27 ga Fabrairu, 2025.
Rahotanni sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun kai farmaki otal din ne, inda suka yi ikirarin cewa jami’an hukumar EFCC ne.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dalori ya karbi ragamar jagorancin jam’iyyar APC a hukumance

Shugaban riko na jam’iyyar APC, Ali Bukar Dalori, ya bukaci shugabanni da mambobin jam’iyyar da su zauna cikin hadin kai bayan murabus din tsohon shugaban...

An dakatar da jirgin Rano Air kan zargin matsalar inji – NCAA

Hukumar kula da sufurin jiragen sama ta Najeriya (NCAA) ta dakatar da wani jirgin Rano Air mai lamba 5N-BZY bayan fuskantar hatsarin gobara da matsalar...

Mafi Shahara