DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu a Abuja ta dakatar da Majalisar Dattawa daga ladabtar da Sanata Natasha

-

 

Sanata Natasha Akpoti

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta dakatar da kwamitin da’a na majalisar dattawa da karbar koken jama’a daga ladabtar da sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan.

Alkalin kotun, Obiora Egwuatu, ya ba da umarnin ne a ranar Talata bayan wata takardar karar da lauyan Akpoti-Uduaghan ya shigar a gaban kotun.

A ranar 20 ga watan Fabrairun shekarar 2025, sanatar mai wakiltar Kogi ta tsakiya ta yi musayar kalamai da shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, kan batun sauyin wurin zama da aka yi mata.

Kin bin umarnin shugaban majalisar Godswill Akpabio da ta yi, ya janyo cece kuce a cikin majalisar da ma wajen majalisar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Zaben Okowa a matsayin abokin takarar Atiku ne kuskuren da ya kayar da PDP a 2023 — Abba Moro

Shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawa, Sanata Abba Moro, ya bayyana cewa zaɓen tsohon gwamnan jihar Delta, Ifeanyi Okowa, a matsayin abokin takarar shugaban ƙasa...

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 kudin ritayarsu

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya kudin fanshon fiye da Naira biliyan 15 ga tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 Wadanda abin ya...

Mafi Shahara