DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Saura kiris a dakatar da ni saboda na bayyana albashin Sanatoci a 2018 – Shehu Sani

-

Shehu Sani

Tsohon sanata mai wakiltar Kaduna ta tsakiya, Shehu Sani, ya bayyana cewa da kyar ya tsallake rijiya, bayan da majalisar dattawa ta yi yunkurin dakatar da shi a shekarar 2018 saboda ya bayyana albashi da alawus-alawus na ‘yan majalisar Dattawa.

A cewar Shehu Sani, ba don shugaban majalisar dattawa na lokacin Bukola Saraki da mataimakinsa Ike Ekweremadu sun sanya baki ba, shima da an dakatar da shi na tsawon watanni shida.

Google search engine

Ya bayyana hakan ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X bayan dakatar da Sanatar Kogi ta tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan.

Jaridar Punch ta rawaito Shehu Sani na cewa, muddin mutum yana cikin majalisa kuma ya fallasa wani abu to babu wani Sanata da zai goyi da bayansa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Jami’an tsaron Chadi hudu sun kwanta dama a wata fafatawa da wasu mahara a arewacin kasar

Lamarin ya faru ne da yammacin ranar 17, ga watan Febarairun da muke ciki a lokacin da wata motar jigilar wani kamfani ke cikin tafiya...

Masu zanga zanga a Sénégal na neman adalci ga dalibin Jami’ar Cheikh Anta Diop ta birnin Dakar da aka halaka

Masu zanga zangar da suka hada da magoya bayan jam'iyya mai mulki ta Pastef sun amsa kiran wata hadaka ce ta dalibai da 'yan fafutikar...

Mafi Shahara