DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Saura kiris a dakatar da ni saboda na bayyana albashin Sanatoci a 2018 – Shehu Sani

-

Shehu Sani

Tsohon sanata mai wakiltar Kaduna ta tsakiya, Shehu Sani, ya bayyana cewa da kyar ya tsallake rijiya, bayan da majalisar dattawa ta yi yunkurin dakatar da shi a shekarar 2018 saboda ya bayyana albashi da alawus-alawus na ‘yan majalisar Dattawa.

A cewar Shehu Sani, ba don shugaban majalisar dattawa na lokacin Bukola Saraki da mataimakinsa Ike Ekweremadu sun sanya baki ba, shima da an dakatar da shi na tsawon watanni shida.

Google search engine

Ya bayyana hakan ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X bayan dakatar da Sanatar Kogi ta tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan.

Jaridar Punch ta rawaito Shehu Sani na cewa, muddin mutum yana cikin majalisa kuma ya fallasa wani abu to babu wani Sanata da zai goyi da bayansa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kotu za ta yanke hukunci kan belin Abubakar Malami a ranar 7 ga Janairu

Kotun Tarayya da ke zama a Abuja ta sanya 7 ga Janairu domin yanke hukunci kan bukatar beli da Abubakar Malami, tsohon Antoni-Janar na Tarayya...

EFCC ta yi watsi da zargin Gwamna Bala Mohammed na tsangwamar jami’an gwamnatinsa

Hukumar EFCC mai yaki da yi wa tattalin arzikin kasa tu'annati a Nijeriya ta yi watsi da ikirarin da Bala Mohammed, Gwamnan Jihar Bauchi, ya yi...

Mafi Shahara