DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Saura kiris a dakatar da ni saboda na bayyana albashin Sanatoci a 2018 – Shehu Sani

-

Shehu Sani

Tsohon sanata mai wakiltar Kaduna ta tsakiya, Shehu Sani, ya bayyana cewa da kyar ya tsallake rijiya, bayan da majalisar dattawa ta yi yunkurin dakatar da shi a shekarar 2018 saboda ya bayyana albashi da alawus-alawus na ‘yan majalisar Dattawa.

A cewar Shehu Sani, ba don shugaban majalisar dattawa na lokacin Bukola Saraki da mataimakinsa Ike Ekweremadu sun sanya baki ba, shima da an dakatar da shi na tsawon watanni shida.

Google search engine

Ya bayyana hakan ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X bayan dakatar da Sanatar Kogi ta tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan.

Jaridar Punch ta rawaito Shehu Sani na cewa, muddin mutum yana cikin majalisa kuma ya fallasa wani abu to babu wani Sanata da zai goyi da bayansa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara