DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An bindige shugaban kungiyar Miyetti Allah na jihar Kwara

-

 

Google search engine

‘Yan bindiga sun bingige shugaban kungiyar Miyetti Allah reshen jihar Kwara, Alhaji Idris Abubakar Sakaina.

Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 10:00 na daren ranar Asabar, da maharan suka harbe shi har lahira a kofar gidansa da ke Oke Ose a birnin Ilorin.

A cewar Jaridar Daily Trust ‘yan bindigar sun bar shi a nan cikin jini ba tare da sun dauki wani abu nasa ba.

Marigayin mai shekaru 32, an ce tsohon mataimaki na musamman ne ga shugaban karamar hukumar Moro kuma shugaban matasan Fulanin jihar Kwara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar dattawan Nijeriya za ta tattauna da shugaba Tinubu kan kalaman Trump

Majalisar dattawan Nijeriya ta bayyana cewa za ta gana da shugaba Tinubu da bangaren zartarwa domin tattauna batun rikicin diflomasiyya da kalaman shugaban Amurka Donald...

ECOWAS ta yi watsi da zargin Trump na halaka mabiya addinin kirista a Nijeriya

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ECOWAS ta fitar da sanarwa mai dauke da watsi kan zargin cewa hare-haren ta’addanci da ke ƙaruwa a...

Mafi Shahara