DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An bindige shugaban kungiyar Miyetti Allah na jihar Kwara

-

 

Google search engine

‘Yan bindiga sun bingige shugaban kungiyar Miyetti Allah reshen jihar Kwara, Alhaji Idris Abubakar Sakaina.

Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 10:00 na daren ranar Asabar, da maharan suka harbe shi har lahira a kofar gidansa da ke Oke Ose a birnin Ilorin.

A cewar Jaridar Daily Trust ‘yan bindigar sun bar shi a nan cikin jini ba tare da sun dauki wani abu nasa ba.

Marigayin mai shekaru 32, an ce tsohon mataimaki na musamman ne ga shugaban karamar hukumar Moro kuma shugaban matasan Fulanin jihar Kwara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnan Kano, Abba Kabir zai koma jam’iyyar APC a ranar Litinin – Sanusi Bature Dawakin Tofa

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, zai koma jam’iyyar APC a hukumance ranar Litinin, 26 ga Janairu 2026, bayan murabus dinsa daga NNPP da...

‘Yan sanda sun hallaka ‘yan bindiga 3 tare da ceto wasu a wasu kauyukan iyakokin jihar Gombe

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe ta tabbatar da hallaka wasu ‘yan bindiga uku tare da kwato makamai da harsasai, sannan ta ceto wasu daga cikin...

Mafi Shahara