DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotun Daukaka Kara ta umurci a dakatar da amfani da hukuncin mayar da Sarki Sanusi sai an ji daga Kotun Koli

-

 

Sarki Sanusi

Google search engine

Kotun daukaka kara ta jingine hukuncin 10 ga watan Janairu da ya amince da halascin  dokar rusa masarautu da gwamnatin Kano ta yi, dokar da ta mayar da Sarki Sunusi kan sarautar Kano.

Jaridar Solacebase ta ruwaito cewa, da suke yanke sabon hukuncin a wannan Juma’a a kotun da ta yi zamanta a Abuja, alkalai uku sun ce mai shari’a Abubakar Liman ya yanke hukuncin ne ba tare da la’akari da cewa kotunsa ba ta da hurumi ba. 

Da yake karin haske kan hukuncin justice Okon Abang ya ce a yanzu kotun ba za ta je uffan ba, har sai ta ji matakin da kotun koli ta  dauka.

Bayan hukuncin kotun daukaka karar na 10 a ga watan Fabrairu, gwamnatin Kano ta garzaya kotun koli da bukatar ta yi fatali da hukuncin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tinubu ya gargadi Alkalan Nijeriya da kada su karkata ga cin hanci ko rashin adalci

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi kira ga alkalai da sauran ma’aikatan shari’a a Najeriya da su ci gaba da zama masu gaskiya, adalci,...

PDP ta musanta zargin kirƙirar sa hannun Sakataren ta na kasa

Kwamitin zartaswa na Ƙasa na jam’iyyar PDP ya musanta zargin ƙirƙirar sa hannu da Sakataren jam’iyyar na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, ya yi. Mai magana da...

Mafi Shahara