DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Rundunar sojin saman Nijeriya ta halaka ‘yan bindiga 20, tare da lalata maboyar su a jihar Katsina

-

 

Rundunar sojin saman Nijeriya ta bayyana cewa, wasu hare-hare ta sama da jami’an tsaro suka kai a jihar Katsina sun lalata maboyar ‘yan ta’adda a dajin Unguwar Goga da ke unguwar Ruwan Godiya a karamar hukumar Faskari ta jihar.

Rundunar sojin karkashin Operation Fansar Yamma ta kai harinne da sanyin safiyar ranar Alhamis, a sansanonin ‘yan bindiga guda biyu, Gero Alhaji da kuma Alhaji Riga.

A wata sanarwa da mataimakin daraktan yada labarai da hulda da jama’a na rundunar sojin saman Nijeriya, Kaftin Kabiru Ali ya fitar a daren Juma’a, ta ce harin da jiragen suka kai sun yi nasarar halaka ‘yan bindiga sama da 20, tare da samun gagarumar nasara a kansu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwamishinan Jigawa ya mayar da rarar Naira miliyan 301 daga kudaden da aka ware don shirin ciyar da al’umma a watan Ramadan

Kwamishinan ayyuka na musamman na jihar Jigawa, Alhaji Auwalu Danladi Sankara, ya mayar da Naira miliyan 301 zuwa baitul malin jihar, daga cikin Naira biliyan...

Gwamnatin mulkin sojin Nijar ta karɓi wasikun kulla kawance daga sabbin jakadun ƙasashe 8

A ranar Juma’a, 9 ga Mayu, 2025, fadar gwamatin ta Jamhuriyar Nijar ta karɓi sabbin jakadun daga jakadun ƙasashen duniya guda takwas. Inda shugaban mulkin sojin...

Mafi Shahara