DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Rundunar sojin saman Nijeriya ta halaka ‘yan bindiga 20, tare da lalata maboyar su a jihar Katsina

-

 

Google search engine

Rundunar sojin saman Nijeriya ta bayyana cewa, wasu hare-hare ta sama da jami’an tsaro suka kai a jihar Katsina sun lalata maboyar ‘yan ta’adda a dajin Unguwar Goga da ke unguwar Ruwan Godiya a karamar hukumar Faskari ta jihar.

Rundunar sojin karkashin Operation Fansar Yamma ta kai harinne da sanyin safiyar ranar Alhamis, a sansanonin ‘yan bindiga guda biyu, Gero Alhaji da kuma Alhaji Riga.

A wata sanarwa da mataimakin daraktan yada labarai da hulda da jama’a na rundunar sojin saman Nijeriya, Kaftin Kabiru Ali ya fitar a daren Juma’a, ta ce harin da jiragen suka kai sun yi nasarar halaka ‘yan bindiga sama da 20, tare da samun gagarumar nasara a kansu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara