DCL Hausa Radio
Kaitsaye

SERAP ta maka Tinubu a kotu kan matakin da ya dauka na dakatar da Gwamnn jihar Rivers, da ‘yan majalisar dokokin jihar

-

Bola Ahmed Tinubu/Sim Fubara

Kungiyar SERAP mai fafutikar yaki da cin hanci da rashawa a Nijeriya ta maka shugaban kasa Bola Tinubu kotu kan dakatar da Gwamnan jihar Rivers Fubara da mataimakiyar sa na tsawon wata shida,abinda ta ce anyi shi ba bisa doka  ba.

SERAP ta yi zargin cewa matakin ya saba wa tanadin tsarin mulki da kuma bata tsarin mulkin dimokradiyyar Nijeriya.

Mambobin kungiyar a jihar Rivers su uku ne suka shigar da karar wacce  aka shigar gaban babbar kotun tarayya da ke Abuja ranar Juma’a.

Daga cikin wadan da ake karar akwai babban lauyan gwamnati  kuma Ministan shari’a, Lateef Fagbemi SAN, da Vice Admiral Ibok-Ete Ibas mai ritaya a matsayin wadanda ake tuhuma.

A cikin wata sanarwa da mataimakin darakta kungiyar Kolawole Oluwadare ya fitar a ranar Lahadi, ta bayar da hujjar cewa matakin na dakatar da zababben gwamnan da ‘yan majalisar jihar take hakkin jama’a ne.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 kudin ritayarsu

Gwamna Abba K. Yusuf ya amince a biya kudin fanshon fiye da Naira biliyan 15 ga tsofaffin Kansilolin gwamnatin Ganduje sama da 3000 Wadanda abin ya...

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da ‘ya’yanta ke yi

PDP za ta tattauna da gwamnoninta kan sauya shekar da 'ya'yanta ke yi nan da makon gobe Kwamitin gudanarwa na kasa (NWC) na jam’iyyar PDP tare da kungiyar gwamnonin...

Mafi Shahara