DCL Hausa Radio
Kaitsaye

SERAP ta maka Tinubu a kotu kan matakin da ya dauka na dakatar da Gwamnn jihar Rivers, da ‘yan majalisar dokokin jihar

-

Bola Ahmed Tinubu/Sim Fubara

Kungiyar SERAP mai fafutikar yaki da cin hanci da rashawa a Nijeriya ta maka shugaban kasa Bola Tinubu kotu kan dakatar da Gwamnan jihar Rivers Fubara da mataimakiyar sa na tsawon wata shida,abinda ta ce anyi shi ba bisa doka  ba.

Google search engine

SERAP ta yi zargin cewa matakin ya saba wa tanadin tsarin mulki da kuma bata tsarin mulkin dimokradiyyar Nijeriya.

Mambobin kungiyar a jihar Rivers su uku ne suka shigar da karar wacce  aka shigar gaban babbar kotun tarayya da ke Abuja ranar Juma’a.

Daga cikin wadan da ake karar akwai babban lauyan gwamnati  kuma Ministan shari’a, Lateef Fagbemi SAN, da Vice Admiral Ibok-Ete Ibas mai ritaya a matsayin wadanda ake tuhuma.

A cikin wata sanarwa da mataimakin darakta kungiyar Kolawole Oluwadare ya fitar a ranar Lahadi, ta bayar da hujjar cewa matakin na dakatar da zababben gwamnan da ‘yan majalisar jihar take hakkin jama’a ne.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An yanke wa ɗan Najeriya hukuncin ɗaurin shekaru 11 a Amurka kan damfara da ta kai dala miliyan 1.3

Wata kotu a Amurka ta yanke wa wani ɗan Najeriya mai zama a San Gabriel Valley, Abiola Femi Quadri, hukuncin ɗaurin shekara 11 da wata...

Natasha ta sake shan alwashin komawa majalisar dattawa a ranar Talata

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, ‘yar Majalisar Dattawa daga jihar Kogi da aka dakatar, ta shigar da ƙara ga Majalisar Dattawa tana neman su girmama hukuncin Babbar...

Mafi Shahara