DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Karancin abinci mai gina jiki da ciwon suga ne ke kara ta’azzara tarin fuka a Nijeriya – Ministan lafiya

-

Farfesa Muhammad Pate 

Ministan lafiya Farfesa Muhammad Pate, ya ce rashin samun wadataccen abinci mai gina jiki da cuta mai karya garkuwar jiki da ciwon suga da shan sigari da kuma shan giya a tsakanin yan shekaru 15 zuwa 44 ne abinda ya fi ta’azzara kamuwa da cutar tarin fuka a Nijeriya.

Farfesa Pate ya bayyana haka ne yayin taron manema labarai a wani bangare na bikin ranar tarin fuka ta duniya, inda yace, Nijeriya tana cikin kasashe goma da suka fi fama da nau’ukan tarin fuka, da kuma masu fama da cuta mai karya garkuwar jiki, yana mai cewa kimanin ‘yan kasar dubu 71 ne suka kamu da cutar tarin fuka a shekarar 2023.

Google search engine

Wani bincike da aka gudanar a shekarar 2017 ya nuna cewa mutum daya ne cikin yan Nijeriya hudu ke da cikakken sani game da illar cutar tarin fuka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Muna da hujja ba a makance muke goyon Tinubu ba – Kungiyar Disciples of Jagaban

Kungiyar magoya bayan shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ta Disciples of Jagaban ta ce ba a makance ta ke nuna goyon baya ga shugaban ba,...

Rundunar sojin Nijeriya ta sulhunta kabilun da ke rikici a Taraba

By Salisu Ado Sulaiman Rundunar sojin kasan Nijeriya ta jagoranci zaman sulhu tsakanin kabilun da ke rikici a jihar Taraba. Kwamandan rundunar Operation Whirl Punch Brigadier Janar...

Mafi Shahara