DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Bankin Duniya ya nuna damuwa bisa rashin ingancin alkaluman ƙididdiga a Nijeriya

-

Tambarin bankin duniya 

Bankin Duniya ya nuna damuwarsa kan yadda Nijeriya ke fitar kididdiga maras inganci, inda ya nuna cewa sauran takwarorinta kamar Mexico da Colombia da Afirka ta Kudu da kuma Brazil sun yi mata fintikau.

Bankin ya bayyana hakan ne yayin wata ziyara da ya kai, karkashin jagorancin Daraktan bankin mai kula da Nijeriya, Ndiame Diop, suka kai wa Ministan kasafin kudi da tsare-tsare Sanata Abubakar Bagudu a ranar Laraba.

A jawabinsa yayin ziyarar Mista John Mistiaen yace tsarin kididdiga na Nijeriya yayi hannun riga na sauran kasashe takwarorinta, inda ya ba da shawarar cewa zuba jarin tsakanin dala miliyan 10 zuwa dala miliyan 15 a ayyukan kididdiga na kasar duk shekara zai inganta aikin sosai tare da daidaita Nijeriya da takwarorinta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Rukunin farko na maniyyatan jihar Bauchi a Nijeriya, sun tashi zuwa Saudiyya- NAHCON

Hukumar aikin Hajji ta Nijeriya ta bayyana cewa maniyyata 2,520 ne daga cikin jihar Bauchi za su halarci aikin Hajjin bana na 2025 a kasar...

An saki ‘Yan jaridar Sahara FM da aka tsare a Agadez

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na nuna cewa an saki ‘yan jarida uku na gidan rediyon Sahara FM da ke Agadez bayan da aka tsare su...

Mafi Shahara