HomeUncategorizedSarkin Kano na 15 Aminu Ado Bayero ya sanar da soke hawan...

Sarkin Kano na 15 Aminu Ado Bayero ya sanar da soke hawan Sallah

-

Alhaji Aminu Ado Bayero 

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya sanar da soke hawan Sallah da aka saba yi duk shekara, kamar yadda aka tsara gudanarwa a baya.

Sarkin ya bayyana hakan ne, a cikin wani takaitaccen faifan bidiyo da ya fitar a daren Laraba, inda ya bayyana dalilan da suka sanya aka dakatar da shirin hawan Sallar.

Ta cikin faifan bidiyon, sarki Aminu, ya bayyana cewa ya bada umarnin soke hawan ne sakamakon kokarin da malaman addinin musulunci da kuma dattawa suka yi wajen ganin an samu zaman lafiya, inda ya bukaci mazauna birnin Kano da su yi amfani da lokacin bikin Sallar wajen ziyartar yan uwa da abokan arziki tare da samun damar halartar bikin Sallah.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

LATEST POSTS

Sarkin Daura ya nada Hamza Sule Sarautar Sadaukin Kasar Hausa

Maimartaba Sarkin Daura Alh Faruk Umar Faruk ya nada Hon. Hamza Sulaiman Faskari Kwamishinan mahallin jihar katsina sarautar Sadaukin Kasar Hausa a fadarsa dake garin...

Kawance domin kayar da Tinubu a 2027 ba zai yi wani tasiri ba, bata lokaci ne kawai, in ji dan jam’iyyar PDP Ayo Fayose

Tsohon gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose, ya yi watsi da gamayyar jam’iyyun adawa na siyasa da ake tattaunawa a kai, da nufin kifar da Gwamnatin...

Babu wanda ya hana Kasshim Shettima shiga fadar Shugaban kasa ta Villa, labarin ba ya da tushe bare makama – Mai magana da yawunsa...

Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Harkokin Yada Labarai Stanley Nkwocha,ya bayyana labarin da ke yawo a kafafan sada zumunta, dangane da hana...

Jiga-jigan APC sun tattaru a Abuja, sun tabbatar wa da Shugaba Tinubu zai yi nasara da gagarumin rinjaye a zaben 2027

Jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki sun gudanar da wani gangami a Abuja, inda suka bayyana cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu zai samu gagarumin rinjaye a...

Most Popular

spot_img