DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sarkin Kano na 15 Aminu Ado Bayero ya sanar da soke hawan Sallah

-

Alhaji Aminu Ado Bayero 

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado Bayero, ya sanar da soke hawan Sallah da aka saba yi duk shekara, kamar yadda aka tsara gudanarwa a baya.

Sarkin ya bayyana hakan ne, a cikin wani takaitaccen faifan bidiyo da ya fitar a daren Laraba, inda ya bayyana dalilan da suka sanya aka dakatar da shirin hawan Sallar.

Ta cikin faifan bidiyon, sarki Aminu, ya bayyana cewa ya bada umarnin soke hawan ne sakamakon kokarin da malaman addinin musulunci da kuma dattawa suka yi wajen ganin an samu zaman lafiya, inda ya bukaci mazauna birnin Kano da su yi amfani da lokacin bikin Sallar wajen ziyartar yan uwa da abokan arziki tare da samun damar halartar bikin Sallah.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Rukunin farko na maniyyatan jihar Bauchi a Nijeriya, sun tashi zuwa Saudiyya- NAHCON

Hukumar aikin Hajji ta Nijeriya ta bayyana cewa maniyyata 2,520 ne daga cikin jihar Bauchi za su halarci aikin Hajjin bana na 2025 a kasar...

An saki ‘Yan jaridar Sahara FM da aka tsare a Agadez

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na nuna cewa an saki ‘yan jarida uku na gidan rediyon Sahara FM da ke Agadez bayan da aka tsare su...

Mafi Shahara