DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaban hukumar aikin Hajji ta Nijeriya NAHCON ya yi alhinin ajalin matafiya 16 a jihar EDO

-

Farfesa Abdullahi Sale Usman

Shugaban hukumar aikin Hajji ta Nijeriya NAHCON, Farfesa Abdullah Sale , ya bayyana bakin cikin sa kan ajalin matafiya mafarauta su 16 da aka kashe a garin Uromi na jihar Edo.

Shugaban ya mika ta’aziyyar sa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da iyalan wadan da suka rasu da al’ummar Nijeriya baki daya.

A cewar shugaban al’ummar Nijeriya ya zama wajibi su mutunta  juna a matsayin ‘yan uwa daya ba tare da banbanci ba don ci gaban kasa , kana kare rayukan kowa ya zama tilas a fadin kasar.

Farfesa Saleh ya ce ya yi matukar kaduwa tare da bakin cikin abinda ya faru na matafiyan a yankin Undune Efandion dake Uromi a jihar ta Edo da ya faru ranar 27 ga Maris 2025.

Haka zalika ya yabawa shugaban kasa Tinubu , bisa umarnin da ya bayar na kama batagarin da sukayi aika – aikar.

Ya kuma yaba da kokarin jami’an tsaro na kama Mutum 14 da suka aikata ta’addancin bisa umarnin na shugaban kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya

An saka ranar da za a fitar da sakamakon binciken zargin alaka da muggan kwayoyi da ya hada da Shugaba Tinubu na Nijeriya. Ana dai...

Za mu iya cin zabenmu ko babu ku, kalaman Elrufa’i ga gwamnonin Nijeriya

  Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa sabuwar kawancen jam’iyyu adawa na da karfin da zai kayar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu...

Mafi Shahara