Babban hafsan hafsoshin tsaron Nijeriya ya yi Allah-wadai da ajalin matafiya-mafarauta da ya faru a jihar Edo

-

CDS Christopher Musa

 

Babban hafsan hafsoshin tsaron Nijeriya, Janar Christopher Musa, ya yi Allah wadai da kisan matafiya a jihar Edo, tare  da shan allwashin hukunta wadanda suka aikata laifin.

A ranar Alhamis din da ta gabata wasu gungun batagari  a garin Uromi na jihar Edo suka yi ajalin wasu matafiya-mafarauta guda 16.

Rahotanni sun bayyana cewa wadanda harin ya rutsa da su na komawa gida ne daga jihar Rivers domin kammala azumin watan Ramadan da kuma Sallar Idi tare da iyalansu a lokacin da aka kai musu harin.

Wannan lamari dai ya sha suka daga kungiyoyi daban-daban na arewacin kasar, da gwamnatocin jihohi, da kuma ‘yan majalisar dokoki.

A wata sanarwa da daraktan yada labarai rundunar ya fitar, Brig.  Janar Tukur Gusau, ya ce da an sanar da hukumomin da suka dace domin tantance sunayen wadanda abin ya shafa.

Cristopher Musa ya yi tir da kira da kakkaudar murya kan kisan da aka yi wa mafarauta, a lokacin da suke kan hanyarsu ta komawa gida  da ya ce tabbas wannan abu ba zai tafi a banza ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun ji takaicin ficewar gwamna Sheriff Oborevwori na jihar Delta daga PDP zuwa APC- Umar Damagum

Shugaban ruko na jam’iyyar PDP na ƙasa, Umar Damagum, ya bayyana ficewar Gwamna Sheriff Oborevwori na Jihar Delta, tare da wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar zuwa...

Talauci zai karu a Najeriya nan da 2027 – Bankin Duniya

Bankin Duniya ya bayyana cewa yawan mutanen Najeriya da ke fama da talauci zai karu nan da shekarar 2027, duk da kasancewar kasar na daga...

Mafi Shahara