DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hedikwatar tsaron Nijeriya ta musanta rahotannin da ke cewa Jamhuriyar Nijar ta fice daga cikin rundunar hadin gwiwar tsaro ta kasa da kasa

-

Christopher Musa

Hedikwatar tsaron Nijeriya ta musanta rahotannin da ke cewa Jamhuriyar Nijar ta fice daga cikin rundunar hadin gwiwar tsaro ta kasa da kasa, inda ta bayyana cewa irin wannan matakin zai haifar da babbar illa ga tsaro.

Da yake jawabi ga manema labarai a Abuja Daraktan yada labarai na hedkwatar tsaro, Manjo Janar Markus Kangye, ya bayyana cewa MNJTF na ci gaba da kasancewa cikin rundunar hadin gwiwar tsaro a yankin, kuma dole ne a yi kokarin hana kowace kasa fita daga tsarin.

Google search engine

Ya ce bayanan da ake yadawa ba gaskiya bane, amma kasashen da ke yankin Tafkin Chadi sun Samar da rundunar hadin gwiwa ta kasa da kasar ne domin magance matsalolin tsaro da ke ci musu tuwo a kwarya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dalori ya karbi ragamar jagorancin jam’iyyar APC a hukumance

Shugaban riko na jam’iyyar APC, Ali Bukar Dalori, ya bukaci shugabanni da mambobin jam’iyyar da su zauna cikin hadin kai bayan murabus din tsohon shugaban...

An dakatar da jirgin Rano Air kan zargin matsalar inji – NCAA

Hukumar kula da sufurin jiragen sama ta Najeriya (NCAA) ta dakatar da wani jirgin Rano Air mai lamba 5N-BZY bayan fuskantar hatsarin gobara da matsalar...

Mafi Shahara